Isa ga babban shafi
Najeriya

Gwamnatin Borno za ta bude manyan hanyoyi

Gwamnatin jihar Borno da ke arewa maso gabashin tarayyar Najeriya ta ce, ta na shirin sake bude manyan hanyoyin da suka hada birnin Maiduguri da sauran sassan jihar.

Gwamnan Jahar borno Kashim shetimma a lokacin da ya ke kai ziyara a Baga inda aka kai harin da ya kashe mutane 185 a Jahar Borno Arewacin Najeriya
Gwamnan Jahar borno Kashim shetimma a lokacin da ya ke kai ziyara a Baga inda aka kai harin da ya kashe mutane 185 a Jahar Borno Arewacin Najeriya REUTERS
Talla

Gwamnan jihar, Kashim Shettima ya bayyana haka a lokacin da ya ke ganawa da 'yan kasuwa da ke gudanar da harkokinsu a kasuwar Monday Market da ke Maiduguri.

Gwamnan ya ce, ya sanar da daukan matakin ne domin farfado da tattalin arzikin jihar wanda ya gamu da koma baya sakamakon hare-haren kungiyar Bokom Haram.

Tuni dai gwamnatin Shettima ta gina shagunan hada hadar kasuwanci a sassan daban daban na babban birnin jihar domin karfafa gwiwar ‘yan kasuwa.

Gwamnan dai ya yi amanna cewa, nan ba da jimawa ba za a kawo karshen kungiyar Boko Haram da ta dade ta na ta’asa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.