Sojan Nigeria sun bude Manyan hanyoyin tafiya Maiduguri.
Rundunar Sojan Nigeria ta bude wasu manyan hanyoyi da ba'a bi saboda matakan tsaro tsakanin birnin Maiduguri jihar Borno zuwa sassan jihar, bayan rufe wadannan hanyoyi na tsawon shekaru uku sakamakon hare-haren da ‘yan kungiyar Boko Haram ke kaiwa jama'a.
Wallafawa ranar:
Babban Hafsan sojan kasa na Nigeria Laftanar Janar Tukur Buratai ya sanar da haka, a garin Damboa, a yayinda yake kaddamar da wasu Babura da sojan zasu rika amfani dasu domin farautar ‘yan kungiyar Boko Haram.
A cewar Laftanar Janar Tukur Buratai sojan za su ci gaba da kokarin kare lafiyar jama'a da dukiyoyin su, inda yace babbar hanya tsakanin Maiduguri zuwa garin Biu an bude ta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu