CAF ta ci tarar Najeriya kan cunkoso a Kaduna
Hukumar kwallon kafa a Afrika CAF ta ci tarar Najeriya kudi dala dubu biyar kan laifin cunkuso da rashin wadaccen tsaro a wasanta da Masar a filin wasan Ahmadu Bello a Kaduna arewacin kasar.
Wallafawa ranar:
An buga wasan ne dai a ranar 29 ga Maris kuma sama da ‘yan kallo dubu Arba’in suka kutsa domin kallon wasan a filin na Kaduna mai daukar ‘yan kallo dubu sha biyar.
Gwamnatin Kaduna dai ta bude kofa ne ga ‘Yan kallo domin shiga kallon wasan kyauta.
Sai dai an tashi wasan ne ci 1 da 1, kafin Masar ta fitar da Najeriya a Alexandria a wasannin neman shiga gasar cin kofin Afrika da za a gudanar a Gabon.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu