Isa ga babban shafi
Amnesty

Amnesty ta bukaci a rufe barikin soji na Giwa

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta yi kira ga gwamnatin Najeriya data gaggauta sakin wasu mutane 1,200 da ake tsare da su a barikin soji na Giwa dake birnin Maiduguri na jahar Borno sannan ta rufe barikin baki daya.

Barikin Giwa dake birnin Maiduguri, a jahar Borno
Barikin Giwa dake birnin Maiduguri, a jahar Borno Getty Images
Talla

Amnesty ta yi kiran ne bayan gano cewar mutane 150 ne suka mutu ciki harda kananan yara 11 da jarirai sakamakon matsaloli da suka kunshi yunwa da kishirwa da kuma cututtuka.

Amnesty ta ce akalla mutane 150 da suka hada da kananan yara ne suka mutu a shekara 2016, a barikin sojin na Giwa.

A rahoton da kungiyar ta fitar yau Laraba, kungiyar ta yi zargin cewa ana tsare da mutanen ne a cikin wani mummunan hali da ya keta hakkin bil’adama.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.