Isa ga babban shafi
Najeriya

Boko Haram ta samu makamai a sansanonin soji- Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce, babu wata kwakkwarar sheda da ke nuna cewa, kungiyar Boko Haram na samun tallafin makamai daga kungiyar ISIS mai da’awar jihadi a yankin gabas ta tsakiya.

Shugaban Najeriya  Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari youtube
Talla

Shugaba Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyin ‘yan jaridu a yayin rufe taron tattauana matsalar Bokon Haram a birnin Abuja .

Shugaban ya kara da cewa, mayakan na Boko Haram, sun samu tarin makamai ne daga sansanonin sojoji da na ‘yan sanda bayan farmakin da suka kaddamar a lokacin da suke kan ganiyar tayar da kayar baya a Najeriya da kasashen da ke makwabtaka da ita.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.