Isa ga babban shafi
Najeriya

Buhari zai je London dan neman magani

Yau litinin Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai fara hutun kwanaki 10 wadda za ta kai shi birnin London dan kula da lafiyarsa.

Muhammadu Buhari, shugaban Najeriya
Muhammadu Buhari, shugaban Najeriya AFP PHOTO / SAJJAD HUSSAIN
Talla

Femi Adeshina mai baiwa shugaba Buhari shawara kan harkokin yada labarai yace tafiyar ta biyo bayan shawarwarin likitoci don samun kula na musamman daga kwararru saboda ciwon kunnen dake damun shugaban.

A baya an yi ta yayata labarin cewar Shugaba Buhari yana fama da jinya daya daga cikin dalilan da suka hana shi ziyara a Ogoniland a Niger Delta mai fama da matsalar barayin mai,  sai dai kuma fadar shugaban ta musanta hakan a wannan lokacin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.