Isa ga babban shafi
Najeriya

Boko Haram ta sace mata a Borno

Rahotanni daga Najeriya sun ce, mayakan kungiyar Boko Haram sun kai sabon hari a wani kauye da ke kusa da garin Chibok na jihar Barno inda suka sace mata guda 3.

Wasu daga cikin 'yan mata Chibok da Boko Haram ta sace a shekara ta 2014
Wasu daga cikin 'yan mata Chibok da Boko Haram ta sace a shekara ta 2014 via CNN
Talla

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayyana cewa,  kungiyar ta kai harin ne a kauyen Kautuva a jiya da asuba, inda ta kona gidaje tare da harbe wasu mazauna garin, kamar yadda wadanda suka tsallake rijiya da baya da kuma 'yan kato da gora suka sheda.

Wani mazaunin garin Ali Pagu ya ce, da kyar suka sha kafin daga bisani su tsere zuwa garin Chibok domin samun mafaka.

A watan Aprilun shekara ta 2014 ne, kungiyar ta Boko Haram ta sace 'yan matan sakandaren garin Chibok fiye da 200, al'amarin da ya janyo cecekuce a duk fadin duniya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.