Isa ga babban shafi
Najeriya

An kama mai barazanar kifar da gwamnatin Buhari

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya ta bayyana Jones Abiri da aka fi sani da Janar Akotebe Darikoro daga yankin Niger Delta a matsayin mutumin da ya yi barazanar kifar da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari tare da kai harin bam a fadarsa da ke Abuja.

Shugaban Najeriya  Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

An dai kama Darikoro ne a Yenagoa da ke jihar Bayelsa yayin da hukumar ta DSS ta bayyana shi a matsayin shugaban wata hadakar kungiya mai fafutukar neman ‘yancin Niger Delta.

Hukumar ta kara da cewa, mutumin ya amsa laifin aikata manyan laifuka da suka hada da kaddamar da hare-hae kan bututun kamfaninonin man fetir, abinda ke jefa tattalin arzikin kasar cikin mawuyacin hali.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.