An kama mai barazanar kifar da gwamnatin Buhari
Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya ta bayyana Jones Abiri da aka fi sani da Janar Akotebe Darikoro daga yankin Niger Delta a matsayin mutumin da ya yi barazanar kifar da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari tare da kai harin bam a fadarsa da ke Abuja.
Wallafawa ranar:
An dai kama Darikoro ne a Yenagoa da ke jihar Bayelsa yayin da hukumar ta DSS ta bayyana shi a matsayin shugaban wata hadakar kungiya mai fafutukar neman ‘yancin Niger Delta.
Hukumar ta kara da cewa, mutumin ya amsa laifin aikata manyan laifuka da suka hada da kaddamar da hare-hae kan bututun kamfaninonin man fetir, abinda ke jefa tattalin arzikin kasar cikin mawuyacin hali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu