Najeriya
Buhari ya gana da Dogara kan badakalar kasafin 2016
Shugaban Majalisar wakilan Najeriya, Yakubu Dogara ya gana da shugaban kasar, Muhammad Buhari kan badakalar cuwa-cuwa a kasafin kudin shekarar 2016.
Wallafawa ranar:
Talla
Bayan ganawarsu a yau a fadar shugaban da ke birnin Abuja, Dogara ya shaida wa manema labarai cewa, ba zai yi murabus daga kujerar sa ba duk kuwa da kiranye-kiranyen da wasu kungiyoyin fararen hula ke yi na ya sauka.
Dogara ya musanta aikata laifin da ake zarginsa da shi na yunkurin shigar da cuwa-cuwar biliyoyin Naira a cikin kasafin ba tare da gudanar da wani aiki ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu