Isa ga babban shafi
Najeriya

Boko Haram ta yi wa sojin Najeriya kwanton-bauna

Akalla sojojin Najeriya da jami’an kato da gora tara ne suka rasa rayukansu sakamakon kwantar-baunar da mayakan Boko Haram suka yi musu a karamar hukumar Damboa da ke jihar Borno ta tarayyar Najeriya.

Sojojin Najeriya da ke sintiri a karamar hukumar Damboa ta jihar Borno a Najeriya
Sojojin Najeriya da ke sintiri a karamar hukumar Damboa ta jihar Borno a Najeriya AFP
Talla

Sojoji 19 ne suka jikkata a sanadiyar farmakin wanda aka kai musu a dai dai lokacin da suke kan hanyarsu ta komawa sansaninsu bayan samamen da suka kai wa Boko Haram a kauyan Ugundiri da ke karamar hukumar Damboa.

Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya, Kanar Sani Usman ya tabbatar da aukuwar lamarin a cikin wata sanarwa da ya fitar,  in da ya ce, tuni aka garzaya da  sojojin da suka riga mu gidan gaskiya zuwa birnin Maiduguri, yayin da kuma jami’an da suka samu rauni ke samun kulawa a asibitin soji.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.