Isa ga babban shafi
Najeriya

Yau Majalisar Najeriya ke tantance Ibrahim Magu

Yau ne Majalisar Dattawan Najeriya ke gudanar da zama na musamman don tantance shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa Ibrahim Magu, kamar yadda mataimakin kakakin Majalisar, Ike Ekweremadu ya sanar.

Ibrahim Magu
Ibrahim Magu
Talla

Wannan na zuwa ne bayan watanni biyar da fadar shugaban kasa ta gabatar da Magu ga Majalisar don amincewa da shi a matsayin shugaban hukumar ta EFCC.

Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Magu a matsayin mukaddashin hukumar EFCC bayan sauke Ibrahim Lamorde a ranar 9 ga watan Nuwamban bara.

Matukar dai aka tabbatar da shi a yau, Magu zai kasasne mutun na hudu da ya shugabanci hukumar bayan Nuhu Ribadu da Farida Waziri da kuma Ibrahim Lamorde

Masu sa ido na kallon matakin tabbatar da shi a matsayin abin da zai ba shi karfin gwiwar ci gaba da dirar mikiya kan barayin dukiyar talakawa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.