Buhari ya koka kan cinkoson mutane a gidajen yari
Shugaban Najeriya Muhd Buhari ya koka kan halin da gidajen yarin kasar ke ciki, lamarin da ya bayyana a matsayin wata matsala ga kimar kasar.
Wallafawa ranar:
A cewar shugaban, da dama daga cikin gidajen yarin na fama da cinkoson mutane da kashi 90 cikin 100.
Shugaba Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da ya gana da tawagar alkalan kasar karkashin jagorancin Mai Shari’a, Walter Onnoghen a fadarsa da ke birnin Abuja a jiya Jumma’a.
Shugaba Buhari ya ce, akwai bukatar samar da sabbin matakan gaggawa don rage cinkoso a gidajen yarin da ke sassan Najeriya.
Shugaban na ganin cewa, daukan matakin na da muhimmaci wajen rage kudaden kula da gidajen yarin da kuma inganta lafiyar mutanen da ke kulle a cikin su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu