Isa ga babban shafi
Najeriya-Lafiya

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da bullar Karanbon Birai

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da samun cutar da ake kamuwa da ita, a dalilin cin naman biri, da ake kira monkeypox, bayan gwajin da akayi sakamakon samun alamun cutar a jihohi 7.

Cutar karanbon biri kenan da aka samu bullarta a wasu sassa na Najeriya, wadda masana kiwon lafiya suka yi ittifakin na samuwa ne sakamakon ta'ammali na naman biri.
Cutar karanbon biri kenan da aka samu bullarta a wasu sassa na Najeriya, wadda masana kiwon lafiya suka yi ittifakin na samuwa ne sakamakon ta'ammali na naman biri. youtube
Talla

Ministan lafiya na kasar Isaac Adewole yace an samu samfurin cutar 17 a Jihar Bayelsa, kuma gwajin da akayi a cibiyar Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya dake Senegal ya tababtar ad cewar cutar ce.

A nata bangaren, ma’aikatar lafiya ta Najeriyar tace mutane 43 ne suka nuna alamun kamuwa da cutar a Jihohi 6 dake Yankin kudancin kasar da suka hada da Legas, sai kuma Abuja daga Arewa.

Yayin zantawarsa da sashin Hausa na RFI, Dr Muhammed Aliyu, na Cibiyar yaki da cututtukan dabbobi dake Vom a Najeriya, yayi mana bayani akan yadda za’a kaucewa kamuwa da cutar.

00:54

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da bullar Kyandar Birai

Bashir Ibrahim Idris

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.