Najeriya zata hada kai da Nijar don magance rikicin manoma da makiyaya
Ministan cikin gida na Najeriya Janar AbduRahaman Dambazau mai ritaya, ya ce gwamnatin kasar zata hada gwiwa da Jamhuriyar Nijar wajen kawo karshen rikicin manoma da makiyaya.
Wallafawa ranar:
Ministan ya bada tabbacin shirin hadin gwiwar ne, a lokacin da tawagar wasu ‘yan majalisar Jamhuriyar ta Nijar ta kai masa ziyara a Abuja.
Jagoran tawagar ‘yan majalisun, Sanusi Mareini, ya koka bisa wasu rahotanni da suek cewa makiyayan da suke kai hare-hare a sassan najeriya sun shigo ne daga Jamhuriyar ta Nijar.
Sai dai Dambazau ya karyata jita-jitar, inda ya bayyana kwarin gwiwar samun nasarar kawancen la’akari da alaka ta Addini da kabila da ke tsakanin kasashen biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu