Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya zata hada kai da Nijar don magance rikicin manoma da makiyaya

Ministan cikin gida na Najeriya Janar AbduRahaman Dambazau mai ritaya, ya ce gwamnatin kasar zata hada gwiwa da Jamhuriyar Nijar wajen kawo karshen rikicin manoma da makiyaya.

Ministan cikin gida na Najeriya, AbdulRahman  Dambazau.
Ministan cikin gida na Najeriya, AbdulRahman Dambazau. guardian.ng
Talla

Ministan ya bada tabbacin shirin hadin gwiwar ne, a lokacin da tawagar wasu ‘yan majalisar Jamhuriyar ta Nijar ta kai masa ziyara a Abuja.

Jagoran tawagar ‘yan majalisun, Sanusi Mareini, ya koka bisa wasu rahotanni da suek cewa makiyayan da suke kai hare-hare a sassan najeriya sun shigo ne daga Jamhuriyar ta Nijar.

Sai dai Dambazau ya karyata jita-jitar, inda ya bayyana kwarin gwiwar samun nasarar kawancen la’akari da alaka ta Addini da kabila da ke tsakanin kasashen biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.