Isa ga babban shafi
Najeriya

Kaduna: Yan sanda sun kubutarda daruruwan mutane daga ukuba

Rundunar 'Yan Sandan jihar Kaduna a tarayyar Najeriya ta samu nasarar ceto wasu mutane kimanin 300 da suka hada da manya da kananan yara, da ake tsare da su a wata makaranta dake unguwar Rigasa, da sunan koyar da tarbiya.

Wasu daga cikin dalibai da jami'an 'Yan Sanda suka ceto daga wata makaranta da ake azabtar da su a jihar Kaduna dake Najeriya.
Wasu daga cikin dalibai da jami'an 'Yan Sanda suka ceto daga wata makaranta da ake azabtar da su a jihar Kaduna dake Najeriya. Reuters
Talla

Rundunar ‘yan sandan ta ce ta kai samamen ne bayan samun rahoton zarge-zarge kan makarantar kan batutuwan da suka shafi azabtarwa da kuma yin lalata da yara maza.

Kakakin ‘yan sandan Yakubu Sabo, ya ce daga cikin wadanda suka ceto akwai kananan yara guda 100 da shekarunsu basu fi tara ba, cikin mari, makare a wani karamin daki a ginin makarantar, da sunan basu tarbiya.

Sai dai shugaban makarantar Malam Isma’il ya musanta zarge-zargen da ake yi wa makarantar.

Wakilinmu a Kaduna, Aminu Sani Sado ya aiko mana rahoto kan wannan al’amari.

Kuna iya latsa alamar sautin dake kasa domin sauraron cikakken rahoton.

03:00

Yan sanda sun bankado wata makaranta da ake cin zarafin dalibai

Aminu Sani Sado

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.