Isa ga babban shafi
Najeriya

Za mu bai wa Buhari izinin karbo bashin Dala biliyan 30-Lawan

Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Ahmad Lawan ya bayyana cewa, Majalisar za a amince da bukatar shugaba Muhammadu Buhari ta karbo rancen Dala biliyan 30.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. REUTERS/Siphiwe Sibeko
Talla

A yayin zanta wa da manema labarai a birnin tarayya Abuja, Sanata Lawan ya ce, Majalisa ta takwas wadda ta gabata, ta ki amincewa da bukatar Buhari ne saboda rashin gabatar mata da cikakkun bayanai a wancan lokaci.

Shugaban Majalisar ya ce, yanzu bangaren zartaswar ya koyi darasi, inda a wannan karo ya gabatar da wasikarsa dauke da cikakkun bayanan ciyo bashin.

Gwamnatin Buhari ta ce, za ta ciyo bashin makudaden kudaden ne domin gudanar da wasu manyan ayyuka a sassan kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.