Isa ga babban shafi
Najeriya-Coronavirus

Hana kwararru gwajin cutar corona a Kogi da Cross River kuskure ne babba - Likitoci

Kungiyar likitocin Najeriya ta nuna takaicinta kan yadda gwamnatocin Cross River da Kogi suka hana cibiyar dake yaki da yaduwar cutuka ta Najeriyar NCDC gudanar da gwaje-gwajen annobar coronavirus a jihohinsu.

Wani jami'in lafiya a Abuja babban birnin Najeriya, yayin yiwa wani mutum gwajin cutar corona a ranar 15 ga Afrilu, 2020.
Wani jami'in lafiya a Abuja babban birnin Najeriya, yayin yiwa wani mutum gwajin cutar corona a ranar 15 ga Afrilu, 2020. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Wannan na zuwa ne bayanda gwamnonin suka yi zargin za a yi amfani da matakin gudanar da gwaje-gwajen wajen shigar musu da cutar.

Yayin zantawa da sashin Hausa na RFI, Dakta Yusuf Abdu Misau, malami a Jami’ar Fasaha ta jami'ar Abubakar Tafawa Balewa dake Bauchi, kuma daya daga cikin kungiyar likitocin Najeriyar, yace bayyana matakin da gwamnonin jihohin na Cross River ta Kogi suka dauka a matsayin kuskure babba.

Dakta Misau yace irin haka taso faruwa a Jihar Kano, inda da da fari mafi rinjayen al’ummar garin ke ganin cutar coronavirus bata shiga jihar ba, amma bayan soma aikin tawagar kwararrun likitoci sai labara ya sha banban, zalika ya zargi gwamnonin Kogi da Cross River da sanya siyasa cikin lamarin.

01:01

Dakta Yusuf Abdu Misau kan matakin jihohin Kogi da Cross River na hana kwararru yiwa mutane gwajin cutar corona

Zainab Ibrahim

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.