Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Malam Nura Saleh kan matakin jami'an hukumar NIMC na shiga yajin aiki dai dai lokacin da ake gaggawar kammala yiwa al'ummar Najeriya katin dan kasa
Wallafawa ranar:
Kunna - 04:12
A yayinda Gwamnatin Najeriya ta dage wajen ganin an samar da katin dan kasa ga dukkan al’ummarta musamman da zummar taimaka wajen inganta tsaro, sai gashi kwatsam ma’aikatan hukumar kula da ke samar da katin sun tsunduma yajin aiki bisa rashin kayan kare lafiya yayin gudanar da aikisu da kuma batun karin kudaden su.Dangane da wannan dambarwa wakilinmu na Abuja Mohammed Sani Abubakar ya tattauna da Malam Nura Sale, wani kwararren a harkar kimiyyar sadarwa zamani.