Isa ga babban shafi
Kano-Najeriya

Abdul-Jabbar makaryaci ne-Ganduje

Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana Malamin addinin Islaman nan, Sheikh Abdul-Jabbar Nasiru Kabara a matsayin makaryaci kuma mayaudari, yana mai musanta ikirarin malamin na cewa Kwamishinan Ilimin jihar ya tabbatar da zaluntar sa.

Sheikh Abdul-Jabbar Nasiru Kabara.
Sheikh Abdul-Jabbar Nasiru Kabara. hausa.legit.ng
Talla

Kuna iya latsa alamar sautin da ke kasa domin sauraren cikakken bayanin Ganduje

01:04

Martanin Ganduje ga Abdul-Jabbar

Jim kadan da dakatar da shi daga gabatar da wa’azi da huduba, Abdul-Jabbar ya shaida wa manema labarai cewa, an yi hira da Kwaminishin Ilimin Jihar Kano wanda ya tabbatar da cewa, an zalunci malamin a cewarsa.

Kuna iya latsa alamar sautin da ke kasa domin sauraren bayanin Abdul-Jabbar.

00:24

Muryar Abdul-Jabbar

Wata majiya ta shaida wa manema labarai cewa, a halin yanzu gwamnatin Kano wadda ta gana da Majalisar Malaman Jihar, ta bukaci malaman da su duba ayoyin Al-Kur’ani da Hadisan Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam don fitar da hukuncin da ya dace kan Abdul-Jabbar.

Dakataccen malamin ya bayyana cewa, malaman jihar Kano sun shigar da siyasa a cikin addinin Musulunci.

Tuni Jami’an tsaro suka killace gidansa da masallacinsa na Ashabul-Kahfi, sannan kuma aka yi masa daurin talala.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.