Isa ga babban shafi
Najeriya-Hakkin dan Adam

NLC ta yi barazanar shiga yajin aiki kan makomar albashin ma'aikata

A Najeriya kuwa kungiyar Kwadagon Najeriya NLC, ta yi gargadin barazanar tafiya yajin aiki, matukar majalisun tarayyar kasar ba su janye kudurin su na sake nazaratar dokar mafi karancin albashi na kasar ba.

Wasu 'ya'yan kungiyar kwadagon Najeriya yayin zanga-zanga a birnin Abuja.
Wasu 'ya'yan kungiyar kwadagon Najeriya yayin zanga-zanga a birnin Abuja. ASSOCIATED PRESS - SUNDAY ALAMBA
Talla

Shugaban kungiyar Ayuba Wabba ne ya bayyana hakan, lokacin da ya ke jawabi gaban daruruwan mambobin kungiyar da suka gudanar da wani tattaki zuwa zauren majalisar.

Wabba ya kuma kwatanta yunkurin zare dokar mafi karancin albashin daga cikin jadawalin dokokin majalisar a matsayin daura damarar yaki da kungiyar kwadagon.

Matukar dai wannan yunkuri na majalisar ya yiwu, to za a baiwa gwamnonin jihohi damar biyan ma’aikatan su abinda suka ga dama a matsayin albashi, ba tare da la’akari da tsarin gwamnatin tarayyar kasar ba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.