Arewacin Najeriya ne kadai 'Yan kabilar Igbo ke da lumana-Ohanaeze
Babbar kungiyar 'Yan kabilar Igbo dake Najeriya ta bayyana cewar babu inda 'ya'an ta ke zaman lumana da kuma gudanar da harakokin su cikin kwanciyar hankali da ya wuce yankin arewacin kasar.
Wallafawa ranar:
Amaechi wanda ya ce akan dan samu matsala nan da can jifa-jifa amma wannan ba wani abinda zai tada hankali bane musamman a kasar da take kokarin cigaba.
Dangane da batun kafa kasar Biafra da wasu 'Yan kabilar Igbo ke fafutuka a kai,Shugaban kungiyar ya ce matsalar rashin ayyukan yi a yankin ya sa wasu daukar wannan matsayi,inda ya kara da cewa a matsayin su na 'Yan kabilar Igbo na 'Yan kasuwa suna matukar bukatar yankin arewa domin habakar sana'oin su.
Amaechi yace duk da fushin da matasa suke da shi da kuma bukatar ballewa daga Najeriya,su bukatar su itace sake fasalin kasar amma ba raba ta,domin babu hanyar da za'a sarrafa kaya a kauyen ku kuma kayi kasuwa kamar yadda ake yi yanzu a kasuwar Alaba dake lagos.
A nashi jawabi Shugaban kungiyar Ohanaeze na kasa George Obiozor ya bayyana cewar 'Yan kabilar Igbo basa yaki da kowa,sai dai suna bukatar ganin an basu hakkin su na 'Yan kasa,kuma suna bukatar zaman lafiya da hadin kai da kowanne bangare.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu