Isa ga babban shafi

Daliban da aka sace a Kaduna sun kubuta daga hannun Yan bindiga

Rahotanni daga Najeriya sun ce daliban Jami’ar Greenfield ta Jihar Kaduna da aka sace ranar 20 ga watan Afrilu sun yi nasarar kubuta daga hannun 'Yan bindigar da suka sace su.

Iyayan daliban da aka sace a Kaduna
Iyayan daliban da aka sace a Kaduna Kola Sulaimon AFP
Talla

Kakakin Jami’ar Kator Yengeh yace dalibai 14 suka kubuta daga hannun Yan bindigar yau asabar ba tare da yin Karin bayani dangane da kudin fansar da aka biya domin kubutar da suba.

Gwamnatin Jihar Kaduna dake Najeriya taki shiga tattaunawa da Yan bindigar domin kubutar da su saboda matsayin da at dauka na kin biyan kudin fansa ga Yan ta’adda.

Rahotanni sun ce yan uwa da iyayen daliban sun yi ta fadi tashi domin tattara kudaden fansar da yan bindigar suka bukata amma ya zuwa yanzu babu tabbacin abin baiwa Yan bindigar kudi ko kuma a’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.