'Yan bindiga sun kashe mutane 88 a kauyuka 8 na Kebbi
A Najeriya ‘yan sanda a Birnin Kebbi sun tabbatar da cewa mutane 88 ne ‘yan bindiga suka kashe a karamar hukumar Danko-Wasagu ta jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin kasar a ranar Alhamis.
Wallafawa ranar:
Kafofin yada labaran kasar sun ruwaito kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Nafiu Abubakar yana cewa kisan ya auku ne a cikin daren Alhamis zuwa Juma’ar nan.
A cewarsa, ko da yake ‘yan sanda na aikin tantance adadin wadanda suka mutu, tuni rundunar ta aike da jami’anta yankin.
Ya ce kashe kashen sun auko ne a kauyukan in Koro, kimpi, Gaya, Dimi, Zutu, Rafin Gora da Iguenge a kaaramar hukumar Danko/Wasagu ta jihar Kebbin.
Idan ba a manta ba, a watan Afrilun wannan shekarar ne ‘yan bindigar suka kashe jami’an ‘yan sanda 9 a karamar hukumar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu