Jiragen yakin Najeriya sun kashe shanu dubu daya
Jiragen yakin sojin Najeriya sun kashe shahu dubu 1 a wasu hare-hare da suka kaddamar kan Fulani a kananan Hukumomin Keana da Doma da ke jihar Nasarawa.
Wallafawa ranar:
Shugabannin Fulanin yankin da wasu daga cikin wadanda lamarin ya shafa, sun shaida wa Jaridar Daily Trust cewa, an kai farmakin ne tsakanin 10 zuwa 13 ga watan Yuni da muke ciki.
Wasu matasan Fulani makiyaya sun samu rauni, sannan sama da shanunsu 500 sun kwarara cikin jihar Benue mai makwabtaka da Nasarawa kuma har yanzu babu duriyarsu.
Rahotanni na cewa, an shafe tsawon sa’o’i uku ana kaddamar da farmakin a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin fargaba, yayin da Fulanin suka tsere daga gidajensu saboda tsoron salwantar rayukansu.
Wata majiya ta ce, jiragen da suka ka harin na karkashin Rundunar Operation Whirl Stroke wadda ke sansanin sojin saman a Najeriya da ke garin Makurdi na jihar Benue.
Kazalika wata majiyar ta ce, wasu ‘yan bindiga ne suka fara harbar jirgin saman sojin Najeriya, abin da ya haddasa kaddamar da harin bama-baman a daukacin yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu