Isa ga babban shafi
Najeriya-TB Joshua

An gudanar da jana'zar Fasto TB Joshua a Legas

An binne gawar  shahararren mai wa’azin kiristancin nan a Najeriya, kuma shugaban cocin Synagogue Church of All Nations (SCOAN), Fasto TB Joshua a Juma’ar nan a harabar cocinsa dake Ikotun a birnin Lagos.

Jana'izar TB Joshua kenan a birnin Legas, Najeriya.
Jana'izar TB Joshua kenan a birnin Legas, Najeriya. ©
Talla

Joshua ya rasu ne bayan wata sujadar da aka yi a cocinsa  a ranar 5 ga watan Yunin wannan shekarar, kwanaki kadan gabanin zagayowar ranar haihuwarsa, inda zai cika shekaru 58.

Kamfanin dillancin labaran najeriya ya ruwaito cewa mutane daga jinsina, al’adu da kasashe dabam dabam ne suka hallara don bai wa marigayi mai wa’azin girmamawa ta karshe.

Kafin a kai ga sanya shi a rami, an yi addu’o’i tare da karatu da fadakarwa daga littafin Bible mai tsarki.

wanda ya yi wa’azia. jana’izar, Stephen Ogedengbe na ikilisiyar e Wisdom of Chapel Ministry, ya yi kira ga Kiristoci da su yi koyi da halayen TB Joshua don samun salama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.