Akalla yankuna 10 'yan bindiga ke kaiwa hari duk rana a Katsina - Masari
Gwamnan Jihar Katsina da ke Najeriya Aminu Bello Masari, ya bayyana damuwa kan yadda ‘yan bindiga ke kai hare hare a kananan hukumomin Jiharsa akalla 10 a kowacce rana, inda suke kashe mutane da kuma yiwa mata fyade.
Wallafawa ranar:
Masari ya koka ne a yayin da ya karbi bakuncin shugaban rundunar sojin kasa Laftanar Janar Faruk Yahya a fadarsa, inda ya bukaci sojojin da sauran jami’an tsaro da su kara kaimi wajen shawo kan matsalar domin komawa barikokin su.
Masari ya ce basa iya bacci saboda irin tashin hankalin da suke fuskanta, ganin irin labaran da suke samu daga kananan hukumomin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu