Isa ga babban shafi
CUTAR-KWALARA

Kwalara ta kashe mutane 60 a Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina dake Najeriya ta sanar da mutuwar mutane 60 sakamakon barkewar cutar kwalara a jihar wadda ta kama mutane sama da 1,400.

Gwaman Jihar Katsina, Aminu Masari
Gwaman Jihar Katsina, Aminu Masari Dandago
Talla

Kwamishinan lafiyar Jihar Yakubu Danja ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da shugabannin kungiyar likitocin Najeriya a birnin Katsina.

Danja yace yanzu haka gwamnatin na raba maganin yaki da cutar kyauta a asibitocin dake jihar domin dakile yaduwar cutar, tare da kuma shelar yadda jama’a zasu kare kan su daga harbuwa da ita.

A makon jiya hukumomin jihohin Sokoto da Zamfara sun sanar da yawan mutanen da suka mutu sakamakon harbuwa da cutar da suka kai 53, 30 daga cikin su sun mutu ne a Jihar Zamfara, yayin da 23 suka mutu a Sokoto.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.