Isa ga babban shafi
Najeriya - Buhari

Buhari ya sake umurtan jami'an tsaro wajen kawo karshen 'Yan bindiga

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya umarci rundunonin Sojin Kasar da su bullo da sabbin hanyoyin yakin da suke yi don murkushe ‘yan Ta’addan da ke garkuwa da jama’a a yankin Arewa maso yamma da Arewa ta Tsakiya cikin gaggawa. Bayyani sun ce a cikin makon nan ne Najeriya za ta sake samun Karin jiragen yaki kirar Super Tucano domin kawo karshen Ta’addanci a fadin kasar. Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron rahoton da wakilinmu Kabiru Yusuf ya aiko mana daga Abuja.

Shugabannin hafsoshin tsaron Najeriya a fadar gawamnatin kasar dake Abuja  yayin ganawar gaggawa kan tsaro ranar 30 ga watan Afrelun 2021 da shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Shugabannin hafsoshin tsaron Najeriya a fadar gawamnatin kasar dake Abuja yayin ganawar gaggawa kan tsaro ranar 30 ga watan Afrelun 2021 da shugaban kasa Muhammadu Buhari. © Presidency of Nigeria
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.