Isa ga babban shafi
Najeriya-Naira

Najeriya za ta kaddamar da Nairar yanar gizo ta eNaira

A Litinin ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai kaddamar da Nairar da za a rika hada hada da ita ta intanet, wato eNaira, a fadarsa da ke babban birnin kasar Abuja, a cewar wata sanarwa da ta fito daga babban bankin kasar ranar Lahadi.

Najeriya za ta kaddamar da makwafen Nairarta ta intanet
Najeriya za ta kaddamar da makwafen Nairarta ta intanet AP - Sunday Alamba
Talla

Wannan na zuwa ne bayan da aka jinkirta kaddamar da Nairar a farkon wannan wata na Oktoba, kuma sanarwar ta kara da cewa Nairar za ta fara aiki a ranar da aka kaddamar da ita.

Kaddamar da wannan Nairar ta intanet za ta sanya Najeriya a cikin sahun gaba na kasashen da suke da kudin yanar gizo a nahiyar Afrika, bayan da Ghana ta kaddamar da fara gwajin kudinta na  eCedi a watan Satumba.

Manyan bankuna a fadin duniya na kokarin samar da makwafin kudadensu na intanet, biyo bayan habakar hada hada ta intanet da kuma yin gogayya da kudin Crypto da kasashe suka gaza sanya ido a kansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.