An samu asarar rayuka sakamakon tashin bam a Kano
Rahotanni daga jihar Kano ta Najeriya na cewa, akwai yiwuwar samun asarar rayukan mutane sakamakon fashewar wani abu da ake zaton bam ne a wata mararrabar hanya da ke kasuwar Sabon-gari a jihar.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban kasuwar ta Sabon-gari Nafi’u Nuhu Ndabo ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho Abubakar Isa Dandago cewa, lallai bisa dukkan alamu, fashewar ta yi kama da tarwatsewar bam, kuma ana zaton wasu kananan yaran makaranta na cikin wadanda suka rasa rayukansu.
Za mu kawo muku karin bayani nan gaba……
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu