Isa ga babban shafi

Najeriya da Birtaniya sun sanya hannu a yarjejeniyar dakile kwararar baki

Najeriya da Birtaniya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar dakile kwararar bakin-haure, wadda a karkashin ta za a rika mayar da wadanda suka tsallaka zuwa kasar Turan ba bisa ka’ida ba, da kuma sauran masu aikata laifuka zuwa gida Najeriya.

Najeriya ta amince da dawo mata da 'yan ciranin da suka shiga Birtaniyar ta barauniyar hanya ko kuma suka aikata wani babban laifi.
Najeriya ta amince da dawo mata da 'yan ciranin da suka shiga Birtaniyar ta barauniyar hanya ko kuma suka aikata wani babban laifi. AP - Yousef Murad
Talla

Tuni dai kashin farko na bakin-hauren da aka kora daga Birtaniya suka bar kasar zuwa Najeriya da Ghana, inda a ranar 30 ga watan Yuni, aka iza keyar ‘yan Najeriya 13 zuwa birnin Legas, sai kuma ‘yan Ghana 8, da suka hada da bakin-haure 5 da masu aikata laifuka 3.

Wata sanarwar ofishin harkokin cikin gidan Birtaniya ta ce an yankewa dukkanin masu laifin da aka kora daga Birtaniya hukuncin daurin shekaru sama da 64 a gidan Yari, idan aka hadasu waje guda.

Daya daga cikin manyan jami’an gwamnatin Birtaniya, ya kara da cewar, a halin da ake ciki an iza keyar mutane sama da 10,000 daga Birtaniyar zuwa kasashensu a tsakanin watan Janairun shekara ta 2019 zuwa Mayu na shekarar 2022.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.