Isa ga babban shafi

Boko Haram ta kashe masu ibada a Masallacin Borno

Mayakan Boko Haram sun kai hari a wani Masallaci da ke jihar Borno ta Najeriya, inda suka kashe babban limamin Gima tare da karin wasu masu ibada.

Wasu mayakan Boko Haram.
Wasu mayakan Boko Haram. AFP
Talla

Kazalika harin wanda ya auku a ranar Juma’a, ya kuma raunata mutane da dama, yayin da ‘yan ta’addar suka mamaye garin Ngulde da ke Karamar Hukumar Askira -Uba ta jihar Bornon.

Mayakan da yawansu ya kai 20, sun kai farmakin ne a sanyin safiyar ranar ta Juma’a , inda suka yi ta bude wuta kan mutanen da suka kammala sallar Asuba a Masallacin.

Har ila yau, mayakan sun yi awon gaba da dabbobi da abinci, sannan suka cinna wa wasu motoci wuta a garin na Ngulde wanda ke kusa da dajin Sambisa.

Boko Haram na ci gaba da kisan mutane babu kakkautawa a Najeriya duk da ikirarin gwamnatin kasar na samun galaba a kan mambobin kungiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.