Isa ga babban shafi

‘Yan sanda 3 sun mutu a harin da 'yan bindiga suka kai wa wani Sanata a Najeriya

Wasu ‘yan sanda sun gamu da ajalinsu a a jiya Lahadi  sakamakon harin da ‘yan sanda suka kai wa wani dan majalisar dattawan Najeriya, Sanata Ifeanyi Ubah, wanda ke wakiltar mazabar Anambra ta Kudu.

Hoton domin misali kan 'yan bindiga.
Hoton domin misali kan 'yan bindiga. © Depositphotos
Talla

‘Yan bindigar sun kai wa ayarin sanatan harin ne a kauyen Enugwu-Ukwu a karamar hukumar Njikoka ta jihar Anambra.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigan sun yi wa ayarin na Uba kwanton bauna ne, inda suka bude musu wuta, har suka kashe ‘yan sandan da ba a kai ga tantance adadinsu ba da ke tsaron lafiyar dan majalisar.

Wata majiya ko ta ce tun da farko ‘yan sandan sun tinkari ‘yan bindigar, inda suka yi musayar  wuta amma duk da haka 3 daga cikin jami’an suka mutu.

Da aka tun tube shi, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da harin a kan sanatan,amma ya ce ba a tantance adadin wadanda suka mutu ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.