Isa ga babban shafi

Mazan Najeriya za su fara zaman jego don taya matansu reno

Gwamnatin Najeriiya ta amince a fara bai wa ma’aika maza hutun kwanaki 14  domin taya matansu da ke zaman-jego reno kamar yadda shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayyar kasar ta sanar.

Mazan za su fara hutun kwanaki 14 don taya matansu reno.
Mazan za su fara hutun kwanaki 14 don taya matansu reno. © The Guardian
Talla

Shugabar ma’aikatan gwamnmatin Dr. Folashede Yemi Esan ta  bayyana haka ne a ranar 25 ga wannan wata na Nuwamba a cikin wata sanarwa da ta fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa, babu namijin da za a ba shi irin wannan hutu fiye da sau daya cikin shekaru biyu, sannan kuma ga haihuwa hudu kacal.

Kazalika za a bada irin wannan hutun ga mutumin da ya dauko karamin yaron da bai wuce watanni hudu da haihuwa ba domin renon sa.

DR. Yemi t a ce, bayar zda irin wannan hutun na da aamuhimmaicni musamman don samar da kdangon kauna tsakanin jaariri ko jaririya ga iyaye maza.  

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.