Sabuwar dokar zaben Najeriya ta bai wa nakasassu damar kada kuri'a
A kokarinta na ganin ba a bar nakasassu a baya ba yayin gudanar da babban zaben da za a yi a Najeriya, hukumar zaben kasar, ta shirya musu taron fadakarwa na musamman don ilmantar da su kan tsare-tsaren zaben, da zummar samun cikakkiyar nasara.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:29
Wannan taro na zuwa ne a daidai lokacin da wasu daga cikin nakasassu ko masu bukata ta musamman a kasar, ke korafin cewa watakila ba za su yi zaben ba, sakamakon sabbin matakai da suke gani sun yi tsauri, da hukumar zaben kasar ta fito da su.
Wakilinmu a Bauchi, Ibrahim Malam Goje da ya halarci taron a Bauchi, ya aiko mana da rahoto kan halin da ake ciki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu