Isa ga babban shafi

Jagororin PDP na gudanar da zanga-zanga a Abuja

A Najeriya, jam’iyyar adawa ta PDP na gudanar da zanga-zanga a babban birnin Tarayyar Abuja don nuna  rashin amincewa da yadda aka gudanar da babban zaben kasar. 

Atiku Abubakar zagaye da magoya bayansa a lokacin da yake kada kuri'a a zaben shugaban kasa na 2023 da ya sha kashi.
Atiku Abubakar zagaye da magoya bayansa a lokacin da yake kada kuri'a a zaben shugaban kasa na 2023 da ya sha kashi. REUTERS - ESA ALEXANDER
Talla

Jagororin jam’iyyar, a wani mataki na nuna goyon baya, sun hade da sauran kusoshin jam’iyyar ciki har da kwamitin amintattu na kungiyar wadanda suka fito wannan zanga zangar. 

Dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar  jam’iyyar, Atiku Abubakar, da shugaban jam’iyyar   Dokta  Iyorchia Ayu da daraktan yakin neman zaben jam’iyyar, gwamna Aminu Waziri Tambuwal na daga cikin masu ruwa da tsaki na PDP da suka fito gangamin a ofishin hukumar zaben kasar. 

Baya ga nuna rashin amincewa da yadda aka gudanar da zaben shugaban kasar, jam’iyyar PDP na jayayya da yadda hukumar zaben kasar ta  ayyana Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar. 

Tun da farko PDP ta bukaci a soke zaben shugaban kasar, a kuma gudanar sabo, sakamakon abin da ta kira kurakurai da aka samu a wasu sassan kasar. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.