Isa ga babban shafi

Zaben Najeriya: Wasu 'yan tsagera sun kona kayayyakin zabe a Bayelsa

Wasu ‘yan tsagera sun karbe, tare da kona kayayyakin zabe na wasu mazabu 3 a jihar Bayelsa dake kudu maso kudancin Najeriya a zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jihohi da ke gudana a kasar a halin yanzu.

Wasu jami'an  hukumar zabe jihar Bayelsa ta Najeriya.
Wasu jami'an hukumar zabe jihar Bayelsa ta Najeriya. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Yanzu haka jami’an hukumar zaben kasar da aka tura aiki a yankin Ogbia sun koma Yenagoa, babban birnin jihar  don su tsira da lafiyarsu ganin yadda ‘yan jagaliya suka rikita yankin.

Rahotanni na nuni da cewa jam’iyyun PDP da na APC na takarar kujerar majalisar dokokin yankin, kuma dukkanin jam’iyyun na neman rinjye a majalisar dokokin jihar, gabanin zaben gwamnan jihar da za a yi a 11 ga watan Nuwamba.

Jami’in wayar da kan al’umma na hukumar zaben jihar Bayelsa din, Mr Wilfred Ifogah, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin.

A lokacin wallafa wannan rahoto, alamu na nuni da cewa zabe ba zai yiwu a mazabar  Ogbia ta 2 ba, duba da cewa jami’an INEC sun riga sun koma Yenagoa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.