Isa ga babban shafi

Mun kwato filaye na tiriliyoyin naira a Kano - Gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano da ke Najeriya ta bayyana cewa ta kwato filaye na tiriliyoyin naira tun bayan da Abba Kabir Yusuf ya karbi mulkin jihar.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf © Aminiya
Talla

Sabuwar gwamnatin ta rushe gine-ginen da ke Otel din Daula da filin idi da kasuwannin Kwari da Wambai da dai sauransu, al'amarin da ya haddasa cece-kuce a ciki da wajen jihar.

Gwamnatin ta zargin tsohuwar gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje da mamaye filaye ba bisa ka'ida ba, zargin da ta musanta tare da bayyana shi a matsayin mara tushe.

Sakataren gwamnatin jihar Dr.Baffa Bichi ne ya sanar cewa, darajar kudin gine-ginen da suka rusa ta kai tiriliyoyin Naira a yayin wata hirarsa da kafar talabijin ta Channels.

Mun kwato filayen da darajarsu ta kai tiriliyoyin naira mallakin gwamnatin jihar Kano da tsohuwar gwamnati ta yi rabon su ga jamianta da iyalai. Filin sallar idi kadai, kudinsa ya kai tiriliyoyin naira. Kudin babu iyaka. Inji Dr. Bichi

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.