Isa ga babban shafi

Davido ya sauke bidiyon da ke izgilanci ga ibadar Musulunci

Shahararren mawakin salon kidan Afro  Beats  a Najeriya, David Adeleke da aka fi sani da Davido ya cire bidiyon wata waka da ya wallafa a shafinsa na dandalin sada zumuntar Twitter, bayan da ya  fuskanci caccaka daga sassa da dama na kasar.

Mawakin Najeriya, David Adedeji Adeleke da aka fi sani da Davido
Mawakin Najeriya, David Adedeji Adeleke da aka fi sani da Davido RFI/Stéphanie Aglietti
Talla

Davido ya wallafa bidiyon wakar  da wani ‘yaronsa’ da ake  kira Lagos Olori  ya yi ne, wanda  ya yi izgilanci ga ibadar Musulunci,  lamarin da bai yi wa al’ummar Musulmi dadi ba.

A ranar Asabar, Davido ya sha suka  daga Musulmai da dama a dandalin sada zumuntar zamani, sakamakon wallafa wannan bidiyo  mai tsawon dakikoki 45 a kafar  Twitter.

Bidiyon, wanda Musulmai da dama suka bayana shi  a matsayin izgilanci ga addininsu, ya nuno wani gungun mutane sanye da jallabiya, cikin suffar ibada suna Sallah, inda kwatsam suka barke da rawa da waka bayan Sallar da suke yi tun da farko.

Sun zargi mawakin da rashin nuna girmamawa  ga addinin Islama, ta wajen hada ibadarsu da rawa da waka, suna mai kira a gare  shi da ya nemi afuwar Musulmai.

Fitaccen jarumin wasan fina finan Hausa, Ali Nuhu na daya  daga cikin dimbim Musulman da suka yi tsokaci a kan wannan batu. Zalika, ‘yan siyasa irinsu Sanata  Shehu Sani da Bashir Ahmad duk sun nuna takaicinsu a kan wannan abu da Davido ya yi.

Yanzu dai an zura ido ne a gani ko Davido zai nemi afuwa a kan wannan bidiyo da ya wallafa, wanda ya janyo cece-kuce.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.