Isa ga babban shafi

Jagoran rikicin kabilanci tsakanin mayakan Boko Haram ya mika kansa ga sojoji

Kwamandan kungiyar Boko Haram da ya haddasa rikicin kabilanci tsakanin mambobin kungiyar, wanda ya yi sanadiyar mutuwar kimanin mayaka 82, ya mika kansa ga sojoji.

Amir Bukkwaram ya mikawa sojoji kansa da iyalinsa da mayakansa da dabbobin da kuma makamansu.
Amir Bukkwaram ya mikawa sojoji kansa da iyalinsa da mayakansa da dabbobin da kuma makamansu. © Afolabi Sotunde/Reuters
Talla

Wata majiyar tsaro ta tabbatarwa jaridar Dairly Trust da ake wallafawa a Najeriya cewar, Amir Bukkwaram ya mikawa sojoji kansa da iyalinsa da mayakansa da dabbobin da kuma makamansu.

A cewar majiyar, kwamandan na daga cikin manyan mayakan kungiyar ta Boko Haram, da ya sanya lungu da sako na yankin Tabkin Chadi.

Majiyar ta ce an kai Amir da mutanensa, sashi na uku na rundunar Operation Hadin kai da ke garin Monguno na jahar Borno.

Idan ba a manta ba, a ranar Alhamis ne labarin rikicin kabiyanci tsakanin mayakan Boko Haram din da ya kaure a tsibitin Bukkwaram ya bayyana, inda kusan 82 suka mutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.