Majalisar Lagos ta tsaya kan bakarta ta yin watsi da kwamishinoni
Shugaban majalisar dokokin jihar Lagos Mudashiru Obasa ya ce babu gudu babu ja da baya dangane da kin amincewa da sunayen mutane 17 daga cikin 39 da gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya tura domin tantance su a matsayin kwamishinoninsa.
Wallafawa ranar:
Obasa ya ce majalisar ta dauki wannan mataki ne domin kare martabar jam’iyar ta APC.
Wannan matakin da 'yan majalisar suka dauka yana neman zame musu matsala.
A zaman majalisar na ranar Litinin, Obasa ya ce babu wata barazana ko hari ko cin mutunci da zai sa su sauya matsayarsu.
Da ma dai al’ummar Musulmi a jihar ta Lagos sun gudanar da zanga-zanga kan yadda suka ce gwamnati ta mayar da su saniyar ware, musamman wajen rabon mukamai, amma hakan bai sa ta sake nazarin lamarin ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu