Isa ga babban shafi

Cibiyar samar da wutar lantarkin Najeriya ta sake durkushewa

Cibiyar samar da wutar lantarkin Najeriya ta sake durkushewa, kwanaki kalilan bayan fuskantar matsalar a kasa da mako guda.

Wasu turakun samar da hasken wutar lantarki a Najeriya.
Wasu turakun samar da hasken wutar lantarki a Najeriya. REUTERS - Akintunde Akinleye
Talla

Bayanai sun ce karfi ko yawan wutar lantarkin da babbar cibiyar ke samarwa ya rikito daga ma’aunin megawatts dubu 3 da 594 da tsakar dare zuwa megawatt 42.7.

Wannan matsala ta zo ne kwanaki biyar bayan da babbar  tashar samar da lantarkin Najeriyar da ake kira da ‘National Grid’ a turance ta durkushe har sau biyu a cikin kimanin sa'o'i 12, lamarin da ya jefa al'ummar kasar cikin duhu.

A waccan lokacin dai mahukunta sun bayyana tashin gobara a daya daga cikin muhimman sassan babbar cibiyar samar da wutar, a matsayin dalilin da ya janyo katsewar wutar lantarkin.

A wannan karon, ma dai an danganta sake rushewar cibiyar lantarkin ne da tashin wata gobara, kamar yadda ministan wutar lantarkin Adebayo Adelabu ya bayyana a shafinsa na X da aka fi sani da Twitter a baya.

Ministan ya ce kwararru na kan kokarin warware matsalar da ta auku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.