Isa ga babban shafi
Nijar

Mutane 16 sun kone kurmus a Nijar

A Jamhuriyar Nijar wata karamar motar fasakwarin man feutr  ta yi sanadiyar mutuwar mutane 17 sakamakon harbin bidinga  da wani jami’in kwastam ya yi  a karamar hukumar Tsauni dake cikin gudumar Matamaye yankin Zinder kan iyaka da Tarrayar Najeriya  a yayinda wasu da dama suka jikata.

Wata karamar mota na cin wuta
Wata karamar mota na cin wuta
Talla

 Al'amarin ya faru ne a lokacin da Jam'ian Kwastam suka yi kokarin dakatar da motar yan fasa kwabrin dake dauke da buburutan man fetur ,bayan direban ya ki tsayawa ne, daya daga cikin jami'an kwastam ya bude wuta da bidinga,inda nan take ta kama da wuta ta kuma fada a cikin wani gida mai cinkoson jama'a a garin na Tsauni.

Nan take Direban da mutane 16 ne suka kone kurmus.

Yanzu haka mahakunta sun sanar da soma gudanar da binciken gano gaskiyar dalilin faruwar hadarin.

A baya dai an sha zargin Jami’an kwastam  da  harbe mutanen  har lahira da sunan yaki da fasakwabri  a kasar ta Jamhuriyar Nijar dake samu  kusan daukacin kudaden shigarta daga haraji.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.