Isa ga babban shafi
Nijar

Jamhuriyyar Nijar zata yi bikin cika shekaru 58

Jamhuriyar Nijar zata gudanar da shagulgulan cikarta shekaru 58 da zamanta Jamhuriya ranar 18 ga watan Disamba mai zuwa, inda a wannan shekara jihar Agadez zata zama mai daukar nauyin shagulgulan, kamar yadda aka zagaya dasu wasu jahohin kasar a baya.

Mai Martaba Sarkin Abzin Ibrahim Ummaru
Mai Martaba Sarkin Abzin Ibrahim Ummaru RfI Hausa/Awwal
Talla

Malam Mahamed Abdulkadir da ake kira Maidalili, dan kungiyar farar hula a kasar, ya kuma shaidawa Sashin Hausa na RFI cewa yayin bikin mutanen Agadez masu sama da shekaru 60 basu taba gani, da ya kunshi nadin sarauta da za’a yiwa Mai Martaba Sarkin Azbin Ibrahim Ummaru, sai kuma wankan sarautar da za’a yi masa.

A cewar Abdulkadir akwai kuma shirin atasaye na gudun sassarfa da za’ayi wanda ya kunshe ‘yan kasashen ketare, domin karfafa zaman lafiya da kuma hadin kai, tsakanin al’ummar Jamhuriyyar Nijar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.