Isa ga babban shafi
NIJAR-ILIMI

Birtaniya ta gayyaci Bazoum taron bunkasa ilimi

Gwamnatin Birtaniya ta gayyaci shugaban Jamhuriyar Bazoum Mohammed domin halartar taro akan harkokin bada ilimi da kasar zata shirya.

Shugaban Nijar Bazoum Mohammed tare da ministan kula da harkokin Afirka na Birtaniya James Duddridge
Shugaban Nijar Bazoum Mohammed tare da ministan kula da harkokin Afirka na Birtaniya James Duddridge © Niger Presidency
Talla

Ministan Birtaniya dake kula da harkokin Afirka James Duddridge ya mika takardar gayyatar ga shugaba Bazoum lokacin da ya ziyarce shi a fadar sa dake birnin Yammai.

Duddridge ya taya shugaban kasar murnar nasarar zaben da aka samu a kasar da kuma mika mulki ba tare da samun wata matsala ba, yayin da suka tattauna kan batutuwa da dama da suka hada da matsalar tsaro a yankin Sahel da tattalin arziki tsakanin kasashen biyu.

Shugaban Nijar Bazoum Mohammed tare da tawagar ministan kula da harkokin Afirka na Birtaniya James Duddridge
Shugaban Nijar Bazoum Mohammed tare da tawagar ministan kula da harkokin Afirka na Birtaniya James Duddridge © Niger Presidency

Bayan ganawar ministan ya bayyana farin cikin sa da amsa gayyatar shiga taron da zai gudana a Birtaniya da shugaba Bazoum yayi musamman saboda yadda gwamnatin sa ke fifita bangaren bada ilimi.

Shugaba Bazoum Mohammed ya sanya batu inganta ilimin mata a cikin manufofin gwamnatin sa domin ganin mata sun daina barin karatu domin yin aure ko kuma yin wasu sana’oi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.