Isa ga babban shafi

Mutane 35 suka mutu sanadiyyar ambaliya a jamhuriyar Nijar

Ruwan sama dai-dai da bakin kwariya da aka soma tun a farkon watan Yuni a Jamhuriyar Nijar sun hadasa mutuwar mutane 35 tareda tilastawa kusan  dubu 26.500 barin matsugunin su.

Ambaliya mai karfin gaske
Ambaliya mai karfin gaske REUTERS/Abdiqani Hassan
Talla

A wani rahoto na baya-bayan nan daga hukumar kare jama’a ta Jamhuriyar Nijar da kamfanin dillanci labaren Faransa ya samu a jiya asabar  mutane 20 ne suka mutu  bayan ruftawar gidajen su.

Ambaliya a babban birnin Yameh dake Jamhuriyar Nijar
Ambaliya a babban birnin Yameh dake Jamhuriyar Nijar AFP/Boureima Hama

Yankunan da abin ya fi muni sun hada da Maradi inda aka samu mutuwar mutane 10,Agadez dake arewacin kasar mutane 10 suka mutu a yankin sai babban birnin kasar Yameh inda aka samu mutuwar mutane 8.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.