Isa ga babban shafi

Wasu 'yan Nijar sun mutu a cikin dajin hamadar Tunisia

An gano gawarwakin mutane 6 mata biyu da kuma kananan yara 4 da aka bayyana cewa ‘yan Nijar ne da suka mutu sakamakon kishirwa a cikin dajin hamadar kasar Tunisia.

Wasu baki yan cin rani a garin Agadez
Wasu baki yan cin rani a garin Agadez BOUREIMA HAMA / AFP
Talla

Hukumar de ke kula da bakin haure ta Majalisar Dinkin duniya OIM, ta ce kusan mutane dubu 6 suka mutu a tekun Meditareniya a kokarin su na ketarawa Turai cikin shekaru 5, duk da cewa an samu ragowar adadin mutanen da ke rasa rayukan su a ‘yan tsakanin nan.Garin Agadez ya kasance wata hanya da bakin ke anfani da ita don cimma burin su.

Wasu daga cikin baki yan cin rani dake kokarin tsallakawa a Jamhuriyar Nijar
Wasu daga cikin baki yan cin rani dake kokarin tsallakawa a Jamhuriyar Nijar AFP

Tsawon shekaru ,hukumomin Nijar na yakar kungiyoyin dake daukar nauyin tsallakawa da irin wadanan mutane,kazalika kasashe irin su Libya,Mauritania da Tunisia a duk kullum  sojojin wadanan kasashe na gano gawarwakin mutane cikin dajin hamadar dake kokarin tsallakawa don neman mafaka ta gari a yankin Turai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.