An kama muggan kwayoyi na cfa miliyan dubu 93 a Nijar
Mahukunta a Jamhuriyar Nijar sun ce daga shekara ta 2015 zuwa farkon wannan shekarar, kasar ta kama miyagun kwayoyi iri daban daban da aka kiyasta kudinsu ya haura cfa milyan dubu 93.
Wallafawa ranar:
A taron manema labaran hadin gwiwa da suka gabatar jiya Litinin a birnin Yamai, minista kuma kakakin gwamnatin kasar ta Nijar, Tidjani Abdoul Kadiri da takwaransa na cikin gida Hamadou Souley, sun bayyana cewa yanzu haka akwai mutane da dama da ke tsare saboda zargin fataucin wadannan kwayoyi.
Minista kuma kakakin gwamnatin kasar Tidjani Abdoul Kadri, ya yi wa wakiliyarmu Rakia Arimi karin bayani.
Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu.
An kama muggan kwayoyi na cfa miliyan dubu 93 a Nijar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu