Isa ga babban shafi

Tawagar Gwamnatin Nijar ta ziyarci garin Tamou

Ministan harakokin cikin gida na Jamhuriyar Nijar Hama Adamou Souley, ya shugabanci babbar tawagar da ta kunshi hafsan hafsoshin soji, da gwamnan Tillabéri, da babban kwamandan tsaron kasa,  suka ziyarci  Tamou a safiyar yau asabar don duba halin da ake ciki, su kuma gane gaskiyar lamarin, biyo bayan harin ta'addancin da aka kai mahakar zinari da Ofishin ‘yan sanda na Tamou a ranar 24 ga Oktoba, 2022, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan sanda biyu .

Ministan cikin gida na Jamhuriyar Nijar Hama Adamou Souley, yayin ziyarar garin Tamou
Ministan cikin gida na Jamhuriyar Nijar Hama Adamou Souley, yayin ziyarar garin Tamou © niger
Talla

Ministan cikin gida ya sheidawa manema labarai cewa za a gudanar da bincike don tabbatar da matsayin wadanda suka jikkata domin bambance masu aikin  ta'addanci da wadanda ba su ba.

Yawancin wuraren hakar gwal a wannan yanki 'yan ta'adda ne ke yawan zuwa, wadanda sukan yi amfani da masu aikin hakar zinare a matsayin mafaka.

Gwamnati dai ta dade tana ba wa kananan hukumomin umarnin gudanar da gangamin wayar da kan jama’a domin gujewa wadannan wuraren boye da kuma daina duk wani nau’i na hadin gwiwa da yan ta’adda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.