Isa ga babban shafi

Cape Verde na adawa da batun tura sojoji kasar Nijar

Shugaban kasar Cape Verde, José Maria Neves, ya ce kasarsa mamba ce a kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS, tana mai adawa da matakin aikewa da soja a Jamhuriyar Nijar.

Taron manyan hafsan sojin kasashen ECOWAS
Taron manyan hafsan sojin kasashen ECOWAS AFP - KOLA SULAIMON
Talla

Duk da cewa kasar tana goyon bayan maido da Shugaba Bazoum a kan karagar mulkin kasar, amma shugaban na Cape Verde ya nuna cewa ba za a iya yin hakan ta hanyar shiga tsakani ba.

Bayan taron na Abuja,shugabannin kungiyar sun yanke shawarar yin amfani da diflomasiya kafin tunanin amfani da karfi soja domin warware wannan matsala a Nijar.

Shugaban kasar José Maria Neves, a jawabin da ya gabatarwa  yan kasar a jiya Juma'a a tsibirin Fogo, ya ce "Dole ne dukkanmu mu yi aiki don maido da tsarin mulki a Nijar ta hanyar sulhu da diflomasiya.

Shugaban kasar Cape Verde  José Maria Neves.
Shugaban kasar Cape Verde José Maria Neves. © RFI/Guillaume Thibault

 

 Shugaban na Cape Verde ya kuma bayyana cewa da wuya kasarsa za ta shiga tsakani  tareda da tura soji idan ECOWAS ta yanke shawarar daukar mataki. "

Shugaban kasar Cote D’Ivoire, Alassane Ouattara da dawowa daga taron Abuja, ya sanar da cewa, baya ga kasarsa, Najeriya da Benin, sun yi alkawarin hada sojoji a cikin wannan tsarin na shiga tsakani.

 

Shugabanin sojojin kasashen ECOWAS
Shugabanin sojojin kasashen ECOWAS © AP - Chinedu Asadu Chinedu Asadu

 

Shugaba Ouattara  ya sanar da wata bataliya ta Cote D’Ivoire  mai yawan sojoji 850 zuwa 1,100 a matsayin gudunmawar rundunar ta ECOWAS da nufin shiga tsakani a Nijar. A halin yanzu, kuma duk da barazanar, ana ci gaba da muhawara game da yiwuwar wannan shiga tare da fuskantar manyan kalubale.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.